Posts

Showing posts from October, 2018

MATSALAR SHA'ANIN TSARO A JIHAR ZAMFARA: BARDEN GALADIMA, ALHAJI BELLO IBRAHIM GUSAU YAYI TSOKACI AKAI

Image
Daga Mohammad K Gusau Jihar Zamfara Jiha ce daga Cikin Jihohin Arewa maso Yammacin Najeriya Wadda a lokuttan baya mune Duk inda muka Shiga ake tambayar mu ya Zamfara ya Shariah kasancewar Jihar mu ce ta Farko Fara Kaddamarda aiki da Shariar musulunchi a hukumance a Duk fadin Afiraka ta yamma. A wancan lokacin mune mukafi kowace Jiha a Najeriya Zaman lafiya, Amma a Yau Babu abunda zamuce sai "INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN" ganin irin yadda Jinin bayin Allah a Kullun yake kwarara a Cikin lungu da sako, Karkara da birane na Jihar Zamfara. INA GIZO KE SAKAR?? A Zaman mu Wadanda muka Shaida kuma suka amince da cewa Babu abun bauta sai Allah, Shi kadai ne ke bada Umurni gare mu Kuma Shine ya Kagi halitta to Haka nan Kuma Wajibin mune mu jibinta mashi dukkan lamarin mu na duniya da Kuma lahira. Mu Waiwaya baya mu gani Shin a baya Haka muke? Mun mance da fadar Allah da yace "Allah Bai musanya baiwar da yayima Mutane har sai idan sune suka musanya da...

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: MUTANEN ZAMFARA NA NEMAN ADDU'AR KU

Image
Daga Abdul Balarabe, Gusau Barayi Yan ta'adda da sun ka addabi karamar hukumar mulki ta Zurmi sun kafa tutoci akan babban titin zirga zirga na motoci wanda ya tashi daga Zurmi zuwa Gurbin bore ta jahar Zamfara Bayan Sun kwashe awanni suna barin Wuta tareda Garkuwa da mutane tsakanin jiya Lahadi zuwa yau Litinin sunyi garkuwa da mutane sama da mutun talatin 30 akan hanyar su ta zuwa bidar abunda suka cida iyalansu Bayan Wannan barayin 'yan ta'adda sunkara shigowa da wani sabon bala'i Wanda idan sukayi garkuwa da mutun ya Allah Namiji ko mace to sai sunyi kokarin bata mashi rayuwa ta hanyar yin Luwadi dashi koya amince ko kada ya amince. Yanzu haka barayin sunsa ma sunan dajin dasuke aje mutane idan sunyi garkuwa dasu ZAMFARA SAMBISA Muna kira Zuwa ga Shugaban kasan Nageriya Muhammadu Buhari, Zamfara muna cikin tashin hankali da tabarbarewar kasuwanci da rashin tsaro wanda har yakai yanzu barayi sun amshi Wani yanki a jahar Zamfara yau Litinin. Muna da ...

AN GANO INDA AKA BUNNE GAWAR JANAR IDRIS ALKALI

Image
Daga Datti Assalafiy Dakarun sojin Nigeria sun gano inda aka bunne gawar Janar Idris Alkali a wani guri mai 'dan tazara da kududdufin da aka jefa motarshi Dazunnan babban Kwamandan rundina ta uku General Officer Commanding (GOC) 3 Division Jos, Manjo Janar Benson Akinroluyo ya bayyana cewa kwararrun karnukan sojoji (sniffer dogs) da kwararrun jami'an tattara bayanan sirrin tsaro sune suka jagoranci gano inda aka bunne gawar Janar Idris Alkali Janar Benson ya kara da cewa matasan yankin bayan sun hallaka Janar Idris Alkali sai suka dauke gawarshi suka kai wannan gurin suka bunne, wadanda ake zargi da hannu wajen hallakashi sun bayyana cewa an sake tone gawar Janar Idris Alkali daga wannan kabarin an kai wani waje, kuma ana cigaba da gudanar da bincike Sojoji mun gode, aci gaba da gudanar da bincike kafin hukunci ya biyo baya. Insha Allahu karshen ta'addancin 'yan ta'addan berom a kudancin Jos ya kusa zama tarihi Yaa Allah Ka Jikan Janar Idris Alk...

BUDADDIYAR WASIKA ZUWA GA GWAMNAN ZAMFARA (A.A.YARI)

Image
Daga Yusuf Muhammad Kadauri Amincin Allah ya tabbata gareka mai girma Gwamna dafatar kana cikin nutsuwa da koshin Lafiya a daidai lokacin da kake karanta wannan sako. Bayan haka, Babban dalilin rubuta wannan sako shi ne TUNATARWA zuwa gareka akan matsayin da Allah ya Dorama na kula da dukiya da Rayuwar Al'umma a Matsayinka na jagoran Al'ummar jihar Zamfara. Nasani cewa kai mai Ilimine, Mai Mulki kuma mai dukiya, Ni kuma ba kowa bane illa TALAKA Wanda yake karkashin mulkinka kuma ban kai ko kusa da matakin Ilimin Addini da na Zamani da Allah ya Albarkaceka dashi ba. Amma ga dukkan Alamu ka manta da nauyin da Allah ya dorama, wanda kuma ka dauki Alkawari dakanka tareda da'fa ALQUR'ANI mai girma cewa zaka kare Al'ummar jihar Zamfara da dukiyoyinsu.  Sai dai kash, duniya ta shaida cewa baka cika wannan Alkawari ba. Yana da Wahala a samu rana daya batareda Rayuwa ta salwantaba sakamakon addabar da Barayi suka yiwa  jihar Zamfara, ana Sace dukiyoyin mutane, ...

ABDULAZIZ YARI YA SHIRYA ZANGA-ZANGAR KIN JININ ADAMS OSHOMOLE A JIHAR ZAMFARA

Image
Daga Sani Ahmad Gusau Gwamnan Jihar Zamfara Abdulaziz Yari Abubakar ya shirya yin zanga-zangar nuna kin jinin shugaban jam'iyyar APC ta kasa wato Kwamared Adams Oshomole gobe 25 ga watan Oktoba na shekarar 2019 a garin Gusau. Wannan ya biyo bayan taron  da wasu gwamnoni 8 suka yi wanda Gwamna ya jagoranta domin domin ganin an cire  shugaban jam'iyyar a ranar Talatar da ta gabata a garin Abuja. Yayin da suka kai kukan su, shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya nuna cikakken goyin bayan shi yadda shugaban jam'iyyar ke gudanar da mulkin shi ya kuma umurci gwamnonin da su koma wajen shugaban jam'iyyar domin samun maslaha akan matsalolin da suka faru  a lokacin zaben fitar da gwani a jihohin su. Rahotannin da muke samu sun nuna cewa Gwamnan ya bada umurnin da a dauko motoci tare da mutane zuwa babban birnin jihar wato Gusau domin gudanar da wannan zanga-zangar ta nuna kin jinin shugaban jam'iyyar  APC na Kasa. Wannan bai rasa nasaba da rashin ba gwamnonin dama da...

MARTANI GA WANI DAN GUDUN HIJIRA (1)

Image
Daga Bulama Adamu Wani Dan gudun Hijira wanda ya fece daga Kauyensu a Jihar Borno tun kimanin 2011 ya samu mafuka a Jihar Katsina yana ta yayata karya da jita-jita cewa wai ba abunda ya chanja akan matsalar tsaro a Jihar Borno. Wannan martani ne gareshi saboda kar yasa wanda basu san halinda aka shiga a wancan lokacin da kuma halinda ake ciki a yanzu su dauki maganarsa abar rikewa. Tsakanin shekara ta 2011 zuwa 2015 an samu gagarumin matsalar tsaronda sai da ta kai kusan kimanin Kananan hukumomi (local governments) goma sha bakwai ne suka koma hannun yan boko haram. Alhamdulillahi cikin ikon Allah yanzu ba wani local government da yake hannunsu. Ba ma wanda suke hannunsu din ba, sai da ta kai ko ina cikin Jihar Borno ya zama abun tsoro ga mazaunin gida da kuma matafiyi saboda komai zai iya faruwa a kowane lokaci.  Mutane sun kasance a cikin tsoro a ko da yaushe walau a gida suke, a kan hanya ko kuma a wajen kasuwancinsu.  Kasuwanninmu, makarantu, Masallatai da coci coc...

RIKICIN SIYASAR JIHAR ZAMFARA YAZO KARSHE: ABDULAZIZ YARI ZAI KOMA JAM'IYYAR SDP

Image
Daga Aliyu B. Musa, Abuja. Ga dukkan alamu rikicin siyasar Jihar Zamfara ya zo karshe bayan yanke shawarar da gwamna me ci yanzu yayi na barin jam'iyyar APC zuwa jam'iyyar SDP wato Social Democratic Party mai alamar Doki. Wannan ya biyo bayan zaman da yayi tare da  jagoran siyasar jihar Zamfara wato Sanata Ahmad Sani Yarima a garin Abuja domim samun sasanci wajen tsayar da 'yan takarkaru ta inda shi Gwamna ya ki amincewa da haka. Gwamnan yace shi ba zai yadda da wannan tsari ba hasali ma ya kai kara a Babbar kotun tarayya dake garin Gusau yana jiran sakamakon shari'ar idan an masa adalchi zai tsaya idan ba'a yi ba zai fice daga jam'iyyar. Rahotannin da muke samu daga jihar Zamfara sun nuna Gwamnan ya fara tura magoya bayan sa su karbi katin shedar zama 'yan jam'iyyar SDP kafin samun sakamakon shari'ar da make gudanarwa. Idan baku manta ba wasu  shugabannin APC na kananan hukumomi guda biyu sun maka hukumar zabe da kuma jam'iyyar...

KISAN MANJO JANAR IDRIS: ABIN BOYE ZAI FITO FILI INSHA ALLAH

Image
Rundinar sojin Nigeria Karkashin jagorancin Brigediya Janar Ibrahim Umar Muhammad wato kwamandan da yake jagorantar binciken bacewar Manjo Janar Idris Muhammad Alkali ta gabatar da mutane 13 ga manenma labarai a birnin Jos wanda ake zargi da masaniya akan bacewar Janar Alkali Birgediya Janar Ibrahim Muhammad yace wadannan mutane 13 da aka kama ba wai ana zarginsu kai tsaye da aikata laifin salwantar da rayuwar Janar Idris Alkali ba, amma sune sukaga lokacin da ake tura motar Janar Idris Alkali a cikin kududdufi, kuma sun san mutanen da suka tura motar, don haka yanzu an mikasu ga rundunar 'yan sanda domin gudanar da bincike, a cewar janar Ibrahim. Muna fatan Allah Ya bankada asirin wadanda suke da alhakkin salwantar da rayuwar Janar Idris Alkali.

DANTAKARA GWAMNAN JIHAR ZAMFARA: AKWAI YIWUWAR UWAR JAM'IYYA TA BADA SUNAN MALAM IBRAHIM WAKKALA KO DAUDA LAWAL DARE.

Image
Labarin da muke samu daga babbar  hedikwatar jam'iyyar APC ta kasa ya nuna cewa akwai yiwuwar ita uwar jam'iyyar ta kada ta fitar da sunan daya daga cikin yan takara guda biyu. Yan takarar sun hada da Malam Ibrahim Wakkala wanda shine mataimakin gwamna mai ci yanzu ko kuma Ma'aikacin bankin  First Bank wato Dr. Dauda Lawal Dare. Uwar jam'iyyar ta kasa tayi haka ne domin kawo sasanci tsakanin yan takarkarun saboda a samu zaman lafiya a jihar bayan kasa gudanar da zaben fidda gwani da akayi wanda rikici ya biyo baya hadda rashin rayuka.

BA SHARRI BANE: GA CIKAKKEN BAYANIN ABUN DA YA FARU

Image
Daga  Datti Assalafiy Babban shugaban cocin Living Faith Church worldwide Bishop David Oyedepo, da babban shugaban cocin Roman Catholic Diocese of Sokoto Bishop Matthew Hassan Kukah (babban aminin Jonah Jang), Sheikh Dr. Ahmad Gumi, Tsohon shugaban Kasa Olusegun Obasanjo, Tsohon Mataimakin shugaban Kasa Atiku Abubkar Wadannan mutane da na lissafa sun hadu suka shiga tattaunawar sirri a masaukin tsohon shugaban Kasa Obasanjo dake Olusegun Obasanjo Presidential Library (OOPL) Oke-Mosan Abeokuta, kuma tattaunawar sirrin sun gabatar da ita ne a tsakar daren da ya gabata Cikin wadanda akayi tattaunar sirrin dasu akwai tsohon gwamnan jihar Ogun da tsohon gwamnan jihar Cross River Gbenga Daniel da Liyel Imoke, da kuma Sanata Ben Bruce da wasu manyan jiga jigan 'yan siyasa na jam'iyyar PDP. To jama'a ni dai zanja hankalinmu, wallahi duk tafiyar da akace an hadata da Bishop Matthew Hassan Kukah na rantse da girman Allah ba tafiyar alheri bace, muna da cikakken masaniya ...

SHIRE-SHIREN KOMAWA PDP: KOGUNAN GUSAU YA GANA DA ATIKU

Image
Dantakarar gwamnan Jihar Zamfara wanda gwamnati ke goyawa baya ya gama da Atiku Abubakar. Minene ra'ayin ku akan wannan?

AN RIKE MA WASU 'YAN MAJALISUN JIHAR ZAMFARA WADANDA BASU GOYON BAYAN GWAMNATI KUDIN ALAWUS

Image
An hana wasu 'yan majalisu  su gudu (4) kudin alawus  na su na watan Agusta saboda ba su bin bayan gwamnati. Rahoton da muka samu ya nuna cewa shugaban masu rinjayen majalisar  dokokin jihar wato Honourable Isah Abdulmumini T/Mafara ne ya bada umurni zuwa ga akawun majalisar na a rike kudaden wadannan yan majalisun. Wadanda aka rike ma alawus din sun hada da: 1. Hon Salisu Musa Tsafe 2.Hon. Dayyabu Adamu Rijiya 3. Hon Mansur Ahmad Bungudu da kuma 4. Hon Abdullahi Muhammad Dansadau. Binciken da muka gudanar ya nuna cewa su dai wadannan yan Majalisa suna cikin bangaren da ke adawa da gwamnati wadanda ake kira da G8. Mun kira lambobin wayoyin shugaban masu rinjaye a majalisar  dokokin amma basu shiga ba domin jin gaskiyar wannan lamari.

GWAMNA ABDULAZIZ YARI ABUBAKAR YA KAMMALA KOMAWA JAM'IYYAR PDP

Image
Gwamna Abdulaziz Yari Abubakar na Jihar Zamfara ya kammala shire-shiren barin jam'iyyar APC zuwa jam'iyyar PDP mai alamar lema. Wannan ya biyo bayan takaddamar da ta dabaibaye jam'iyyar APC na fitar da 'yan takara tun daga Gwamna, Sanatoci, 'yan majalisun tarayya da kuma na jiha. Wani na hannun damar shi da ya bukaci a boye sunan shi yace Gwamnan yana kokawa  da rashin adalci da yace uwar jam'iyya ta kasa bata mashi. Idan baku manta ba gwamnan ya sha yin barazana  ga jami'an zabe da uwar jam'iyyar ta turo wajen gudanar da zaben tare da shi kan shi shugaban jam'iyyar na kasa wato Kwamared Adams Oshomole.

LISSAFIN KILISSAFIN KIDAYAR KUDIN DA AKA SALWANTAR A GURIN ZABEN FITAR DA GWANI NA JAM'IYYAR PDP

Image
Daga Datti Assalafiy Akwai a kalla masu zaben fitar da gwani na jam'iyyyar PDP da ya gudana a jihar Rivers daleget mutum dubu hudu (4,000), Bukola Saraki ya baiwa kowani daleget daga cikinsu dalar amurka dubu daya ($1,000) idan aka canza zuwa kudin Nigeria zai koma naira dubu dari uku da hamsin (N350,000), don haka ya sayi delaget dalar amurka dubu hudu  ($4Million) wanda idan aka canza da kudin Nigeria ya zama naira biliyon daya da miliyoyin dari hudu (N1.4 Billion) adadin lissafin kudin da ya baiwa delaget kenan Shi kuma Atiku Abubakar ya baiwa kowani delaget dalar amurka dubu biyar ($5,000) idan aka canza da kudin Nigeria ya koma naira miliyon daya da dubu dari bakwai da hamsin (N1,750,000) a kowani delaget, adadin kudin da ya kashe shine dalar amurka miliyon ashirin ($20,000,000) wanda idan aka canza da kudin Nigeria ya zama naira biliyon bakwai (N7 Billion) adadin kudin da ya kashe kenan Gwamnan jihar Rivers Nyesom Wike shi kuma ya baiwa kowani delaget dalar amu...

ZABEN FIDDA GWANI NA DAN TAKARAR GWAMNA A JIHAR ZAMFARA: GWAMNATI TA KASHE ZUNZURUTUN KUDI HAR NAIRA BILIYAN TAKWAS (8)

Image
Gwamnatin jihar Zamfara ta kashe kudi har Naira Biliyan Takwas (8) wurin zaben fitar da gwani da ba'a ci nasarar  gudanar dashi ba har zuwa lokacin da hukumar zabe ta kasa ta rufe amsar sunan dan yan takara daga jam'iyyu  a fadin kasar. Wani daya daga cikin jami'an jam'iyyar APC da ya bukaci a boye sunan sa da yafito daga karamar hukumar Gumi dake cikin Jihar ya bayyana haka a yayin hira da wakilin mu dake can jihar Zamfara. Ya tabbatar mashi da cewa duk karamar hukumar da take jihar ta amshi kudi har miliyan Dari sau biyu yayin gudanar da zaben. Kashi na farko shine zaben da babban baturen zaben da ka turo daga Abuja  ya soke saboda magudi da aka tafka yayin zaben. Kashi na biyu shine kudaden da aka raba lokacin zaben da aka tashi gudanarwa a jiya Lahadi wanda zaben bai yiwu ba saboda rikici da ya Barker tsakanin yan takarar da gwamnati ke Goya ma baya da kuma na kungiyar G8.

'YAN TA'ADDAN BEROM SUNA YUNKURIN BOYE GASKIYA GAME DA BACEWAR JANAR IDRIS ALKALI

Image
Daga Shafin Datti Assalafiy Sakamakon mamayar garin Dura-Du da dakarun sojin Nigeria sukayi, shugabannin kabilar berom da kungiyoyinsu wadanda suka hada da: -Berom Educational and Cultural Organization (BECO) -Berom Youth Moulders Association (BYMA) -Berom Women Development Association (BEWDA) Sun hadu sun rubuta takardan koke (petition) da sa hannun wakilansu Ngwo Florence Jambol, Da Davou Davou, Choji Dalyop inda suke mika kokensu game da mamayar da sojoji sukayi musu cewa rundinar Operation Safe Haven (OPSH) karkashin kagorancin Manjo Janar Augustine Agundu tana yiwa rayuwarsu barazana A cikin tardan koken sunce babban kwamandan rundinar Operation Save Haven Manjo Janar Augustine ya kira babban basaraken Dura-Du har zuwa ofishinsa a birnin Jos, yace masa ya bashi lokaci kankani yana umartanshi da ya fadawa mutanenshi su fito da gawar Janar Idris Alkali ko kuma su fuskanci fushin sojoji, abinda kwamandan sojin ya fadawa basaraken kenan kawai sai ya tashi ya fice daga offi...

FADA YA BARKE TSAKANIN MASU NEMAN KUJERAR GWAMNA A JIHAR ZAMFARA DA MASU TAKARA BANGAREN GWAMNATI

A wani zama da akeyi na sasanci a wani otal  mai suna City King Hotel dake garin Gusau Babban birnin jihar Zamfara, fada ya barke tsakanin yan takarar da ke da goyon bayan gwamnati da kuma yan kungiyar da ake kira da G8. An fara fadan  ne sakamakon musun da yayi zafi tsakanin Sanata Kabiru Garba Marafa, sanata mai wakiltar Zamfara ta tsakiya da kuma Ikira Aliyu Bilbis wanda tsohon minista ne a lokacin gwamnati Obasanjo. Daga karshe babban darakta  na hukumar tsaro ta farin kaya ya shiga tsakani  inda ya fitar da Sanata Marafa ya dauke shi zuwa ofishin su dake kan hanyar Lalan dake garin Gusau. Idan baku manta ba yau ne ranar karshe da hukumar zabe ta kasa ta kayyade wajen bada sunayen yan takarar da zasu wakilci kowace jam'iyya a kakar zaben da za'a yi a shekarar 2019.

KIRANA ZUWA GA MAI GIRMA GWAMNAN JIHAR ZAMFARA

Image
Daga Malam Aminu Aliyu Gusau. Mai girma ka sani cewar yadda musulunci ya yi horo ga talakkawa da su yi hakuri da shugaban da basu so har Allah Ya kawar da shi  haka ma ya yi horo da kada a dorawa mutane shugaban da basu so . Annabi (saw) ya ce :" Mafi alkhairin shugaba shine wanda ya ke son jama'arsa suma suna sonshi , yana yi masu kyakkyawar addu'ah , suma suna yi mashi . Mafi sharrin shugaba shine wanda yake kin jama'arsa suma suna kinsa , yana yi masu mummunar addu'ah suma suna yi mashi " .  Annabi (saw) ya ce daga cikin mutane uku abi zargi akwai Limamin da yake jagorantar mutane Sallah alhalin su basu sonshi . Wannan a Sallah kenan , balle a jagorancin al'ummah . Mai girma Gwamna rantsuwar da ka yi cewar kwamiti ba zai shigo ba ya gudanar da zabe koda za ka mutu , da kiran da ka yi a fito a yi zanga-zanga duka ba daidai bane ga shugaba , ka yi kuskure . Ka tuna fa da 'yan tawaye suka zagaye gidan Sayyiduna Usman ya dauki matakin han...