ABDULAZIZ YARI YA SHIRYA ZANGA-ZANGAR KIN JININ ADAMS OSHOMOLE A JIHAR ZAMFARA


Daga Sani Ahmad Gusau


Gwamnan Jihar Zamfara Abdulaziz Yari Abubakar ya shirya yin zanga-zangar nuna kin jinin shugaban jam'iyyar APC ta kasa wato Kwamared Adams Oshomole gobe 25 ga watan Oktoba na shekarar 2019 a garin Gusau.


Wannan ya biyo bayan taron  da wasu gwamnoni 8 suka yi wanda Gwamna ya jagoranta domin domin ganin an cire  shugaban jam'iyyar a ranar Talatar da ta gabata a garin Abuja.

Yayin da suka kai kukan su, shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya nuna cikakken goyin bayan shi yadda shugaban jam'iyyar ke gudanar da mulkin shi ya kuma umurci gwamnonin da su koma wajen shugaban jam'iyyar domin samun maslaha akan matsalolin da suka faru  a lokacin zaben fitar da gwani a jihohin su.

Rahotannin da muke samu sun nuna cewa Gwamnan ya bada umurnin da a dauko motoci tare da mutane zuwa babban birnin jihar wato Gusau domin gudanar da wannan zanga-zangar ta nuna kin jinin shugaban jam'iyyar  APC na Kasa. Wannan bai rasa nasaba da rashin ba gwamnonin dama da bai yi ba na suyi yadda suke so wajen tsayar da 'yan takarkarun da suke  so.

Comments

Popular posts from this blog

MUKTAR IDRIS KO SANUSI RIKIJI: AN SAMU RARRABUWAR KAWUNA A CIKIN MAGOYA BAYAN GWAMNATIN ZAMFARA

BA SHARRI BANE: GA CIKAKKEN BAYANIN ABUN DA YA FARU

WANI TSOHON DANMAJALISAR DOKOKIN JIHAR ZAMFARA YAYI WA TSOHON GWAMNA SUJADA