FADA YA BARKE TSAKANIN MASU NEMAN KUJERAR GWAMNA A JIHAR ZAMFARA DA MASU TAKARA BANGAREN GWAMNATI




A wani zama da akeyi na sasanci a wani otal  mai suna City King Hotel dake garin Gusau Babban birnin jihar Zamfara, fada ya barke tsakanin yan takarar da ke da goyon bayan gwamnati da kuma yan kungiyar da ake kira da G8.

An fara fadan  ne sakamakon musun da yayi zafi tsakanin Sanata Kabiru Garba Marafa, sanata mai wakiltar Zamfara ta tsakiya da kuma Ikira Aliyu Bilbis wanda tsohon minista ne a lokacin gwamnati Obasanjo.

Daga karshe babban darakta  na hukumar tsaro ta farin kaya ya shiga tsakani  inda ya fitar da Sanata Marafa ya dauke shi zuwa ofishin su dake kan hanyar Lalan dake garin Gusau.

Idan baku manta ba yau ne ranar karshe da hukumar zabe ta kasa ta kayyade wajen bada sunayen yan takarar da zasu wakilci kowace jam'iyya a kakar zaben da za'a yi a shekarar 2019.




Comments

Popular posts from this blog

MUKTAR IDRIS KO SANUSI RIKIJI: AN SAMU RARRABUWAR KAWUNA A CIKIN MAGOYA BAYAN GWAMNATIN ZAMFARA

BA SHARRI BANE: GA CIKAKKEN BAYANIN ABUN DA YA FARU

WANI TSOHON DANMAJALISAR DOKOKIN JIHAR ZAMFARA YAYI WA TSOHON GWAMNA SUJADA