Posts

Showing posts from September, 2022

Attajirin da ake zargi da yanka dubban mutane a Rwanda zai gurfana a kotu.

Image
  Daya daga cikin manyan mutane na karshe da ake zargi a kisan kiyashin da aka yi a Rwanda a 1994 zai gurfana a gaban kotun duniya da ke birnin Hague a ranar Alhamis. Felicien Kabuga na fuskantar tuhumar aikata kisan kiyashi da laifukan cin zarafin bil-Adama, a kan irin rawar da ake zargin ya taka wajen yanka 'yan kabilar Tutsi da 'yan Hutu masu sassaucin ra'ayi har dubu dari takwas (800,000). A farkon gurfanarsa gaban kotun a 2020, lauyoyin Mista Kabuga, sun musanta laifukan da ake tuhumarsa da su. Ana sa ran ya gurfana da kansa a gaban kotun ta duniya a zaman na Alhamis. Tsawon gomman shekaru Felicien Kabuga ya kasance daya daga cikin mutanen da ake nema a duniya ruwa a jallo. Masu gabatar da kara sun ce Mista Kabuga na gudanar da wata tashar rediyo, wadda ta rika yada kalaman kyama da haddasa gaba, wadanda ake bayyana 'yan kabilar Tutsi a matsayin kyankyasai tare da angiza 'yan Hutu kan su hallaka su duk inda suka gansu. Ana kuma tuhumar mutumin da ya taba kasanc...

Yan Fashin Daji Sun Halaka Basarake Da Wasu Mutane 13 A Jihar Nejan Najer

Image
  Har yanzu dai ‘yan fashin daji na ci gaba da kai hare-hare da kisan jama’a a wasu yankuna na Jihar Nejan Najeriya, wannan dai yana zuwa ne a daidai lokacin kakar debe amfanin gona ke kawo jiki.   Rahotanni daga yankin karamar hukumar Mariga mai Iyaka da Jihohin Zamfara da Kebbi na nuna cewa a karshen makon nan ‘yan fashin dajin sun hallaka basaraken garin Mohoro tare da wasu mutane kimanin 12, saboda basaraken yaki amincewa mutanen yankinsa su biya harajin da ‘yan bindiga suka dorawa mutanen yankin. Gwamnatin Jihar Neja dai tayi Allah wadai da wannan mugun aiki, sakataren gwamnatin Jihar Nejan Alhaji Ahmed Ibrahim Matane ya ce sun tura karin jami’an tsaro a yankin, kuma ya zuwa yanzu hankali ya fara kwantawa a wajen. Ita ma rundunar ‘yan sanda ta Jihar Neja ta tabbatar da aukuwar lamarin, kuma kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Monday Bala Kuryas ya ce suna daukar mataki. A yanzu dai akwai fargaba sosai musamman wajan debe amfanin gona a wadannan yankuna.

Dubun Wani Dan Damfara Mai Canjawa Mutane ATM A Wajen Cirar Kudi Ta Cika A Kano.

Image
Dubun wani matashi mai zamba a bakin ATM dake fadin jihar Kano ta cika a yayi da yayi yunkurin cire wasu kudi daga ATM din da ya canza daga hannun wani. Shedun gani da ido sun ga wasu mutane suna ragargaza wannan matashin,  da suka tambaya sai ake bayyana masu abin da ke faruwa. " Wannan da kuke gani, sune masu zuwa ATM machine suna yiwa mutane wayo su chanja musu ATM din su, su kewaya zuwa wajen masu POS suce cire kudaden dake cikin asusun ajiyar". Ganau din ya kara da cewa, "sun zo wajen mu a Kundila, sun yi withdrawing 450,000 da dare, wayewar gari sai ga Jami'an Yan sanda daga daga CID sun zo an kama mu saboda wata Hajiya tayi korafin an chanja mata ATM an Kuma kwashe mata kudi har Miliyan daya da Ravi. "Muna ta kokarin warware wannan matsalar da muka shiga sai Jiya da dare ya sake zuwa zai cire 150,000 da ATM na wani (Nasiru Hassan, access bank) dama mun gane shi nan aka kama shi, ba musu yace ga kudin mu 450,000 mu rufa masa asiri bai san za a zo bincike s...

Taƙaddama ta ɓarke a APC bayan fitar da ƴan kwamitin yaƙin zaɓen 2023

Image
  Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta yi ƙarin haske game da cece-ku-cen da ake yi musamman a shafukan sada zumunta na internet kan jerin sunayen tawagar yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa da ta fitar. Ƙananan maganganu sun fara ɓulla ne bayan da aka ga babu sunayen wasu jiga-jigan jam'iyyar a cikin jerin sunayen, ciki kuwa har da mataimakin shugaban ƙasa Yemi Osinbajo - wani abu da masana ke ganin zai iya barin baya da ƙura. Bala Ibrahim shi ne Daraktan yaɗa Labaran Jam'iyyar kuma ya ce ba lalle bane a ga sunan kowa da kowa a cikin jerin sunayen mambobin kwamitin saboda "an kafa kwamiti ne domin taimakawa, kuma ba wai ana nufin mutum ɗaya shi zai iya komai ba, inda ka ji an ce mataimaki, akwai wani sama da shi," "A wannan kwamiti an duba an ga babu sunan shugaban ƙasa?, idan akwai shugaban ƙasa, maganar mataimaki ya shigo ba ta taso ba," a cewar Bala Ibrahim. A cewarsa, an kafa kwamitin domin tsara dabarun neman ƙuri'ar ƴan Najeriya saboda akwai buƙat...

DAN A DAI DAITA SAHU YA HADU DA AJALIN SA A YAYIN DA YAKE GUDUN TSERE WA YANSANDA

Image
  Ana zargin wani direba Adai-daita Sahu ya gamu da ajalin sa, a safiyar Asabar  yayin da yake gudun tserewa ƴan sanda dake kula da bin dokar tsaftar Muhalli ta karshen wata wata da gwamnatin jihar ta tanadar. Al'amarin dai ya faru ne a dai-dai gadar Ado Bayero da ake kira gadar Lado dake Gyadi-gyadi a jihar Kano. Ganau sun shaida faruwar lamarin sunce, direban baburin Adai-daita Sahun ya ɗaukko kayan miya ne daga kasuwar ƴan kaba, inda a ƙoƙarin sa na gujewa ƴan sandan da suka biyo shi baburin ya kife wanda hakan yayi sanadiyyar rasa ran nasa. Sai dai kuma har izuwa yanzu rundunar ƴan sandan Kano ba tace komai ba an tuntubi mai magana da yawun rundunar yan sanda ta wayar tarho  amma bai dauki kira ko bada amsar sakon da ya  aike masa ba.