Posts

Showing posts from November, 2019

Ministan Yan Sanda Dingyadi da Sanata Wamakko da Tsohon Gwamna Yari na kitsa shirin haddasa rashin tsaro a Zamfara.

Image
Daga Shafin Maniyarzamfara.com Tsohon gwamna Abdul'aziz Yari Abubakar a ran Larba ta wannan makon yayi wani taron sirri da Ministan Yan Sanda kasa Muhammadu Maigari Dingyadi tare da shugaban kwamitin tsaro Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko a gidan Wamakko dake Asokoro, garin Abuja tare da manufar zargin da akeyi na neman a dauke Kwamishinan Yan Sanda na Jihar Zamfara Muhammadu Dangogo. Bayanin wata majiyar ta baiyana taron na sirri da aka mayar da sunan ziyara ga tsohon gwamna Wamakko yana da manufar hargitsa zaman lafiya na jihar Zamfara don cimma burinsu ga samun iko a matakin tsaro. Anji cewar tsohon gwamna Yari ya yiwa Ministan alkawalin tallafi da samar masa da wasu makudan kudade akan ya tabbatar da Sufeton Yan Sanda yabi umurninsa don dauke kwamishinan Yan Sanda tare da kawo nasu dake yanzu haka a hedikwatar Yan Sanda ta kasa bayan karin girman da akayi masa. Sanata Wamakko shine Shugaban kwamitin tsaro na Majalisar Dattawa yayin da ake zargin yana da hannu akan...

ABDUL'AZIZ YARI DA MAKAFIN MAGOYA BAYAN SHI NA SIYASA

Image
Rubutawa: Mohammed Kabir (MK) Fassarawa: Ibrahim Bello (Alhajin APC) A duk Lokacinda naci Karo da wasu rubuce rubuce na "Ya 'yan jam'iyyar adawa a Jihar Zamfara, abun yana matukar daure mani Kai har inkasa fahimtar Ko cewa wai ko sunsan abunda ake cema adawa da matsayin yan adawa. Ba da dadewa ba, Gwamna Bello Matawalle ya bada gargadi ga tsohon Gwamna Abdul Aziz Yari akan cewa duk ya kuskura ya shigo jihar Zamfara kuma ya kasance aka samu Yan bindiga sunkai hari a wani wuri, Shi Gwamnan da kanshi zai jagoranci jami'an tsaro a kamo Shi.  Kafin wannan Jawabin nashi, Ya bayyana dalilanshi na daukar Wannan Matakin. Ya fahimci cewa duk Lokacinda Abdul Aziz Yari ya shigo a jihar Zamfara to dole Sai ka ji ankai hari Wani gari inda zaka taradda anyi hasarar rayuka da dama, Wanda yake cewa wannan abun dubawa ne ace duk ya shigo Sai wani abu ya faru a cikin jiha? Abunda ya bani Mamaki, Naci Karo da wasu rubuce rubuce na wasu Makafin magoya bayan tsohon Gwamna wada...

BUDADDIYAR WASIKA ZUWA GA MAI DARAJA GWAMNAN JIHAR ZAMFARA HON DR BELLO MUHAMMAD MATAWALLEN MARADUN MON

Image
Daga Alhajin APC Salamun Alaikum. Mai Girma Gwamna tareda Girmamawa da Mutumtawa nake rubuta maka wannan Wasika a matsayinka na Shugaban mu Wanda Allah ya jibantama nauyin Kare rayuwa, mutumci da dukiyoyin Al'ummar jihar Zamfara Samada mutum Miliyan Uku da doriya. Mai Girma Gwamna a Lokacinda Allah ya baka jagorancin Wannan jihar, mutanen jiha sunyi murna da farin ciki Marar misaltuwa musamman mutanen Karkara wadanda sune sukafi Shafuwa da iftila'in dake addabar jihar Zamfara. Tabbas Mai daraja Gwamna Al'ummar jihar Zamfara sunyi farin ciki da jawabinka na farko Wanda a cikin Shi ka nuna damuwarka akan abunda ke faruwa a yankunan jihar Zamfara da kuma irin Matakan daka dauka nayin Sulhu da "Yan bindiga, matakinda ya haifar da d'a Mai ido, Wanda har Shugaban Kasa Muhammad Buhari ya yabama Wannan kokarin naka tareda jinjina maka tareda yin Kira ga takwarorinka Gwamnoni da Suyi koyi dakai ta wannan haujin. Mai Girma Gwamna Saninka ne kuma Sanin al'...

NAMIJIN GORO DA AMFANONINSA GA LAFIYAR DAN ADAM.

Image
(1) YANA KASHE DAFIN MACIJI: Namijin goro yana kashe dafin cizon maciji, idan maciji ya ciji mutum to a bashi namijin goro guda daya ya ci, insha'Allahu nan take zai kashe dafin cizon macijin. (2) YANA KASHE MACIJI: Ana shanya namijin goro ya bushe sai a daka, a barbada a wajen da ba a so macijin ya shiga, idan macijin ya ketara wannan garin namijin goron to nan take zai mutu. (3) YANA KASHE GUBA: Duk wanda ya sha wata guba da gan-gan ko bisa kuskure, a basu namijin goro kwara daya ya cinye, insha'Allah zai amayar da gubar da ya sha. (4)YANA FITAR DA DUK WANI CUTA: Ana yayyanka namijin goro a jika a rika sha, insha'Allah duk wata gubar da ke jikin mutum za ta fita. (5)YANA KARA KARFI: Ana cin namijin goro saboda da karin karfi ga masu iyalai 'yan mintuna Karin a je ga iyalan. (6)YANA MAGANIN CIWON GABABUWA: Cin Namijin goro na magance matsalar ciwon gabobi, kamar yawan gullewa da zugi, yana kuma rage kowane irin radadin azaba. (7)YANA MAGANIN (STD)...

GINA JAMI'A MALLAKAR GWAMNATIN JIHAR ZAMFARA, YA ABUN YAKE TUN FARKO?

Image
Daga Alhajin APC   BAKI MAI YANKE WUYA . Tsohon gwamnan jihar Zamfara Abdulaziz Yari ya tabbatarma duniya da cewa Gina jami'a a Zamfara bashida Wani Muhimmanci, a wata dogowar fira da a kayi da shi a gidan Rediyon Tarayya na Kaduna a 2012. " Jami'a ba itace Matsalar Jihar Zamfara Ba, Inji Abdulaziz Yari" Hujjojin da Audu Yari ya bayar na rashin Muhimmancin Gina Jami'a a jihar Zamfara sune: ✅Jihar Zamfara titi ne matsalar su ba gina Jami'a ba. ✅Hujjar Shi ta biyu itace Wai daliban jihar Zamfara baza su amfana da Jami'ar ba idan an gina ta, kasancewar basa cika gurabin su a Jami'o'in da muke Makwabtaka da su kamar Usmanu Danfodiyo University, B.U.K, ABU, F.U.K (Dutsin ma) da Makamantan su. Lokacinda Audu Yari ke wannan hirar rankatakaf din Najeriya jihar muce batada irin wannan jami'ar, a haka Audu Yari ya kafe kafafuwan Shi cewa lallai baza'ayi Jami'a ba, Allah Manyasha'u Sai Ya Kaddari Tsohon Shugaban Kasa Good...