DUK DA ODAR DA BABBAN KOTUN JIHAR ZAMFARA TA BADA: MAJALISAR DOKOKIN JIHAR ZAMFARA TA RIKE MA WASU YAN MAJALISA ALAWUS

.


Daga S. Sadiq, Gusau.


Alamu ya nuna cewa Majalisar dokokin Jihar Zamfara bata yi amfani da odar da Babban Kotun Jihar Zamfara ta bayar ba karkashin jagorancin Alkali Bello Aliyu Gusau.



Rahotannin da muke samu sun nuna cewa akwai wasu hakkokan su da aka rike masu wadanda suka kun shi alawus nasu da suke karba daga Ma'aikatar kananan hukumomi.

A wani rahoton kuma ya nuna cewa Majalisar dokokin ta kuduri rike masu  alawus wanda ake kira da suna C.A wato Cash Allocation kenan a turance.

Da ya ke hira da wani lauya mai zaman kan shi a Gusau Babban Brinin Jihar, Barrister Rabiu Magaji ya ce Babbar Kotun na da hurumin da zata dauki kwakkwaran mataki na hukunta duk wani mai sa hannu wajen rike masu hakkokin.

Lauyan ya kara da cewa bijirewa odar babban laifi ne wanda yana iya jawo hukunci mai tsanani.

Comments

Popular posts from this blog

MUKTAR IDRIS KO SANUSI RIKIJI: AN SAMU RARRABUWAR KAWUNA A CIKIN MAGOYA BAYAN GWAMNATIN ZAMFARA

BA SHARRI BANE: GA CIKAKKEN BAYANIN ABUN DA YA FARU

WANI TSOHON DANMAJALISAR DOKOKIN JIHAR ZAMFARA YAYI WA TSOHON GWAMNA SUJADA