"YAN MAJALISAR DOKOKIN DA MAJALISAR TA DAKATAR BA KAN KA'IDA BA SUN GANA DA MASU YADA LABARAI




Daga S. Sadiq, Gusau.




" Yan Majalisar dokokin Jihar Zamfara da aka dakata  ba bisa kan doka  ba sun yi taro da masu yada labarai yau 4/01/2019 a garin Gusau.

Da yake magana a madadin "Yan Majalisar, Hon. Salisu Musa Tsafe ya karanta matsayar  su yace ba komi bane dalilin dakatar dasu a Majalisar sai saboda turjiya da suka yi na rashin amincewa  da yi ma Kundin tsarin mulkin na Kasa karan tsaye.

Hon. Salisu ya kawo dalilai daga cikin Kundin tsarin mulki na cewa tsawaita lokacin Chiyamoma na jihar an yi shi ne ba bisa  ka'ida ba. Haka kuma yace doka bata bada damar kara wa duk wani zababbe lokaci ba sai dai Kantomomi.

Game da dakatar dasu, Hon Salisu yace an dakatar dasu ne ba bisa doka ba saboda kafin a dakatar da su sai an kafa kwamitin bincike  da kuma sauraren korafin su.

A nasu  bangaren, wanda ya gabatar da kudurin wato Hon. Isah Abdulmumini T/Mafara ya zayyano laifuka guda Uku  da yasa suka dakatar dasu. Laifukan sun hada da wasu labarai da jaridar Tauraruwa ta kawo na maganar rike masu wasu hakkokan su tare da maganar zargin cin hanci na Miliyan Dari Biyu.

Da yake karin haske kan maganar, Hon Abdullahi Muhammed Dansadau yace hukuncin da aka dauka ya nuna cewa Kakakin Majalisar wato Rt Sanusi Garba Rikiji bai san makamar aiki ba.

Comments

Popular posts from this blog

MUKTAR IDRIS KO SANUSI RIKIJI: AN SAMU RARRABUWAR KAWUNA A CIKIN MAGOYA BAYAN GWAMNATIN ZAMFARA

BA SHARRI BANE: GA CIKAKKEN BAYANIN ABUN DA YA FARU

WANI TSOHON DANMAJALISAR DOKOKIN JIHAR ZAMFARA YAYI WA TSOHON GWAMNA SUJADA