SHIRIN TSIGE MATAIMAKIN GWAMNAN ZAMFARA: MAJALISAR DOKOKI TA DAKATAR DA YAN MAJALISA MASU GOYON BAYAN SA




Daga S. Sadiq, Gusau.

Majalisar dokokin jihar Zamfara a karkashin jogirancin Hon Rt Sanusi Garba Rikiji ta dakatar da 'Yan majalisar dokokin Jihar masu goyon bayan mataimakin Gwamnan Jihar har su Gudu (4).

A zaman ta na yau Alhamis 3/1/2019 wanda Shugaban majalisar ya jagoranta, Hon. Isah Abdulmumini T/Mafara ya gabatar da kuduri na dakatar da wadannan 'Yan majalisu guda gudu (4).



Yan Majalisun sun hada da Hon. Abdullahi Muhammed Dansadau wanda shine mai tsawatarwa na majalisar kuma mai wakiltar Maru ta Kudu, sai kuma Hon. Malam Mani Masaba, Hon. Mansur Ahmad Musa Bungudu Mai wakiltar Bungudu ta Yamma tare da Hon. Salisu Musa Tsafe Kainuwa Dan Majalisa  mai wakiltar Tsafe ta Gabas.

Binciken da jaridar Tauraruwa tayi ya nuna cewa, dakatar da su bai rasa alaka da goyon bayan kugiyar nan ta G8 wadda tayi turjiya game da yunkurin Gwamnan jihar na dauki dora da  ya so yayi.

Wata majiya da muka samu kuma tace Shugabannin majalisar suna jin tsoron idan Gwamna ya kawo kasafin kudi na shekarar bana a majalisar wadannan Yan majalisar suna iya kin aminta da shi.

Comments

Popular posts from this blog

MUKTAR IDRIS KO SANUSI RIKIJI: AN SAMU RARRABUWAR KAWUNA A CIKIN MAGOYA BAYAN GWAMNATIN ZAMFARA

BA SHARRI BANE: GA CIKAKKEN BAYANIN ABUN DA YA FARU

WANI TSOHON DANMAJALISAR DOKOKIN JIHAR ZAMFARA YAYI WA TSOHON GWAMNA SUJADA