SHIRE-SHIREN TSIGE MATAIMAKIN GWAMNA: YAN MAJALISAR DOKOKIN JIHAR ZAMFARA MASU GOYON BAYAN GWAMNATI SUN RARRABA MUKAMAI




Daga S. Sadiq, Gusau.




A shire-shiren ta na tsige mataimakin gwamnan Jihar Zamfara, Majalisar dokokin Jihar Zamfara ta yi rabe-raben mukamai tsakanin "Yan majalisun.

Bayanan sirri da muka samu sun nuna cewa bayan sun kammala shire-shiren zasu gabatar da kuduri na tsige mataimakin gwamnan wato Malam Ibrahim Wakkala Muhammad.

"Yan majalisar masu goyon bayan gwamnati sun tsara mukaman kamar haka:

1. Rt. Hon Sanusi Garba Rikiji wanda shine Kakakin Majalisar dokokin zai je a matsayin Mataimakin  Gwamna.

2. Hon. Isah Abdulmumini Talata Mafara shine shugaban masu rinjaye a Majalisar zai je a matsayin Kakakin Majalisar.

3. Hon. Aliyu Ango Kagara zai je a matsayin shugaban masu tsawatarwa.

4. Hon. Mohammadu Gummi Wanda shine mataimakin Kakakin Majalisar zai je a matsayin   shugaba Kwamitin ma'aikatar kananan hukumomi.

Idan baku manta ba Majalisar dokokin karkashin jagorancin Rt Hon Sanusi Garba Rikiji ta dakatar da wasu  "Yan majalisa guda 4 masu rajin kare muradun talakawan Jihar Zamfara.

Comments

Post a Comment

Popular posts from this blog

MUKTAR IDRIS KO SANUSI RIKIJI: AN SAMU RARRABUWAR KAWUNA A CIKIN MAGOYA BAYAN GWAMNATIN ZAMFARA

BA SHARRI BANE: GA CIKAKKEN BAYANIN ABUN DA YA FARU

WANI TSOHON DANMAJALISAR DOKOKIN JIHAR ZAMFARA YAYI WA TSOHON GWAMNA SUJADA