GWAMNAN JIHAR ZAMFARA YA NISANTA KAN SA DA HANNU WAJEN DAKATAR DA YAN MAJALISU 4



Daga Aliyu B. Musa, Abuja.




Gwamnan Jihar Zamfara Abdulaziz Yari Abubakar ya nisantar da kan sa da sa hannu wajen dakatar da 'yan Majalisar dokokin Jihar Zamfara guda hudu da Majalisar tayi karkashin jagorancin Rt Hon Sanusi Garba Rikiji a satin da ya gabata.

Wannan ya biyo bayan ganawar sirri da yayi tare da Sanata mai wakiltar Zamfara ta yamma kuma Babban jigo a siyasar Zamfara wato Sanata Ahmad Sani Yarima a gidanshi dake Abuja.

Gwamnan ya kuma bukaci Sanata Yarima da ya kira wadannan 'yan Majalisu domin basu hakuri  akan abunda ya faru wanda anyi shi ne ba bisa ka ka'ida ko doka ba.

Rahotannin da muke samu a yau sun nuna wadannan 'yan Majalisun suna Babban Birnin tarayya wato Abuja domin ganawar sirri da shi Sanata Ahmad Sani Yarima.

Comments

Popular posts from this blog

MUKTAR IDRIS KO SANUSI RIKIJI: AN SAMU RARRABUWAR KAWUNA A CIKIN MAGOYA BAYAN GWAMNATIN ZAMFARA

BA SHARRI BANE: GA CIKAKKEN BAYANIN ABUN DA YA FARU

WANI TSOHON DANMAJALISAR DOKOKIN JIHAR ZAMFARA YAYI WA TSOHON GWAMNA SUJADA