JAM'IYYAR APC TA KASA ZATA HUKUNTA GWAMNAN ZAMFARA DA WASU GWAMNONI GUDA UKU




Daga AbdulNasir Bello




Jam'iyyar APC ta kasa ta sha alwashin daukar hukunci mai tsanani akan Gwamnan Jihar Zamfara Abdulaziz Yari Abubakar, Rochas  Okorocha, Amosun da kuma Akeredoku na jihar Ondo sakamakon rashin biyayya da suke ma uwar jam'iyyar.

Idan baku manta ba, a cikin watan da ya gabata ne jam'iyyar APC ta nada  wani kwamiti na tuntuba da neman sasanci wajen 'ya'yan jam'iyyar da suke tunanin ba'a yi masu daidai ba amma wadannan gwamnonin suka yi biris  da matakin.

Da yake magana da kafafen yada  labarai, shugaban kwamitin ya ce shugaban Jam'iyyar APC ta Kasa Kwamared Adams Oshomole zai kafa kwamitin ladabtarwa domin duba ayukkan wasu masu ruwa da tsaki na jam'iyyar musamman Gwamnonin da suke bada goyon  bayan wadanda suke tare dasu da su shiga wata jam'iyya.

Ya kara da cewa jam'iyyar APC ta gaji da yadda wadannan gwamnonin suke mata zagon kasa wajen ganin sake samun nasarar Shugaba Buhari zango na biyu inda ta kara da cewa lokaci yayi da zata cire bara-gurbi domin samun nasara.

Comments

Post a Comment

Popular posts from this blog

MUKTAR IDRIS KO SANUSI RIKIJI: AN SAMU RARRABUWAR KAWUNA A CIKIN MAGOYA BAYAN GWAMNATIN ZAMFARA

BA SHARRI BANE: GA CIKAKKEN BAYANIN ABUN DA YA FARU

WANI TSOHON DANMAJALISAR DOKOKIN JIHAR ZAMFARA YAYI WA TSOHON GWAMNA SUJADA