JIHAR ZAMFARA TANA BUKATAR ADALCHI DAGA GWAMNATIN TARAYYA
Daga Shafin Yasir Ramadan Gwale
A jiya Alhamis fadar Shugaban kasa ta sanar da cewar Shugaba Muhammadu Buhari ya amince a kashe Naira biliyan goma don tallafawa iyalan wadan da suka rasa 'yan uwansu a kashe kashen da aka yi a jihar filato.
Anan nake amfani da wannan dama nayi kira ga Shugaban kasa da yaji tsoron Allah, ya sani zai kasance abin tuhuma a gaban Allah kan nauyin da aka dora masa na al'ummar Najeriya.
Shugaban kasa ya sani babu wani ran dan Najerya da yafi wani. An kashe mutane bila adadun a jihad Zamfara fiye da wannan da ya faru a jihad Fikato, an kashe a Birnin Gwari an kashe a Taraba an kashe a gurare da dama.
Amma duk wadancan kashe kashe da suka auku musamman na Zamfara ba su da kimar da Shugaban kasa zai taimakawa iyalansu da biliyan goma? Shugaban kasa kaji tsoron Allah, babu wanda yafi wani a wajenka a matsayinka na Shugaban kasa.
Bai kamata Shugaban da aka fi yi masa zaton kamanta gaskiya da adalci ya dinga nuna wqriya irin wannan ba, lallai muna kira ga Shugaban kasa yadda aka warewa mutanan jihar Filato biliyan goma suma na jihar Zamfara da aka yi musu kashe kashe a ware musu biliyan goma.
Ifan Shugaban kasa yayi haka ya tabbata shi mai son kamanta gaskiya ne da adalci, rashin yin haka kuwq, nuna fifikon wasu al'umma ne akan wasu, wanda bai kamaci Shugaban kasa yayi haka ba.
Sannan muna kuma kira da a dayki dukkan matakan da suka dace domin kare alfarmar rayukan 'yan Najeriya a ko ina suke. Allah ya bamu lafiya da zama lafiya, ya baiwa Shugabanninmu ikon kqmanta adalci.
A jiya Alhamis fadar Shugaban kasa ta sanar da cewar Shugaba Muhammadu Buhari ya amince a kashe Naira biliyan goma don tallafawa iyalan wadan da suka rasa 'yan uwansu a kashe kashen da aka yi a jihar filato.
Anan nake amfani da wannan dama nayi kira ga Shugaban kasa da yaji tsoron Allah, ya sani zai kasance abin tuhuma a gaban Allah kan nauyin da aka dora masa na al'ummar Najeriya.
Shugaban kasa ya sani babu wani ran dan Najerya da yafi wani. An kashe mutane bila adadun a jihad Zamfara fiye da wannan da ya faru a jihad Fikato, an kashe a Birnin Gwari an kashe a Taraba an kashe a gurare da dama.
Amma duk wadancan kashe kashe da suka auku musamman na Zamfara ba su da kimar da Shugaban kasa zai taimakawa iyalansu da biliyan goma? Shugaban kasa kaji tsoron Allah, babu wanda yafi wani a wajenka a matsayinka na Shugaban kasa.
Bai kamata Shugaban da aka fi yi masa zaton kamanta gaskiya da adalci ya dinga nuna wqriya irin wannan ba, lallai muna kira ga Shugaban kasa yadda aka warewa mutanan jihar Filato biliyan goma suma na jihar Zamfara da aka yi musu kashe kashe a ware musu biliyan goma.
Ifan Shugaban kasa yayi haka ya tabbata shi mai son kamanta gaskiya ne da adalci, rashin yin haka kuwq, nuna fifikon wasu al'umma ne akan wasu, wanda bai kamaci Shugaban kasa yayi haka ba.
Sannan muna kuma kira da a dayki dukkan matakan da suka dace domin kare alfarmar rayukan 'yan Najeriya a ko ina suke. Allah ya bamu lafiya da zama lafiya, ya baiwa Shugabanninmu ikon kqmanta adalci.
Comments
Post a Comment