Posts

Showing posts from October, 2020

SHUGABA BUHARI DA HAUSAWA

Image
  Daga Muhammad Bin Ibrahim Zuwa yanzu, abin da ke bayyana a tsakanin Hausawa, al'ummar da ta nuna qulafucin so ga Shugaba Muhammadu Buhari fiye da yadda ta nuna wa kowane mahaluki a duniya, shi ne nadama. Nadama a kan zaben tumun daren da suka yi. Saboda sun farga cewa abin da suka tsammana a tattare da shi ba haka ba ne. Yanayin nadama mummuna ne, don haka wanda ya samu kansa a ciki abin tausayi ne koda kuwa da gangan ya sa kansa tun a tashin fari. Sai dai kuma, kamar yadda kowane yanayi mai kyau yake da bangarensa mara kyau, haka ma kowane yanayi mara kyau yake da bangare mai kyau. Halin da mu Hausawa muke ciki a yau game da batun shugabanci, hali ne mara kyau da dadi, don mun fi sauran al'ummomin qasar fuskantar uquba, amma kuma halin yana tattare da guzirin busharar farin ciki a gare mu in har muka yarda muka amfana da yanayin ta hanyar tsara lamurranmu da kyau. Yanzu mun gane cewa, gaskiyar mutum ko da'awar gaskiyarsa, ba su ne kadai ababen buqata ga shugaba mai kaman...

AREWA MU FARKA

Image
Daga Muhammad Abba. 1. Akwai son zuciya da kin aminta da gaskiya indai har ba daga bakin ka ko naka ta fito ba. 2. A matsayin mu na musulmai muna danganta komai da addini,  muna wuce iyaka, shiyasa malamai yan Scope suke wasa da hankulan mu. 3. Har yanzu mun kasa gane cewa democradiya ba addini bace, shiyasa yan Arewa ke yakan kawunan su lokacin siyasa. 4. Shuwagabannin Arewa basu damu da talaka ba, abinda ya dame su shine aljihunan su. 5. Masarautu sun koma mabarata, maroka kuma yan maula shiyasa basu fada aji, domin a Arewa ne kadai dan siyasa ke wasa da masarauta yanda yake so, Chairman ma sai ya tumbuke sarki ya zauna lafiya, a kudu kuwa karyan shugaban kasa ya raina masarautar da tafi ko wacce kankanta. 6. A arewa siyasa ta kan makantar da mutum, shiyasa ko ana kashe makwabcin sa, indai har bata shafe shi ba, bazai fito ya kalubalanci hakan ba, har sai kaga wani yana yabon shugaba da ke ci sobida yana amfana da jam'iya ko soyayya marar amfani. Da dai sauran su. Idan dan arewa ...

A SHIRYE MUKE MU YAKI DUK DAN KUDUN DA YA KE SON KIFAR DA GWAMNATIN BUHARI TA AMFANI DA ZANGA-ZANGAR ENDSARS

Image
  Shettima Yerima Shugaban kungiyar matasan Arewa, Yerima Shettima, yace 'yan Arewa baza su rike hannuwan su suna kallon 'yan Kudu su tsige shugaban kasa Muhammadu Buhari akan mulkin Najeriya ba. Da yake zantawa da 'yan jaridu a Minna babban birnin jihar Neja, Shettima ya ce 'yan Kudu suna neman su kara cutar da 'yan  Arewa kamar yadda suka yi bayan mutuwar Umaru Musa Yar'Adua.  Ya kuma bayyana shirin 'yan Arewa dangane da fitowa yaki idan har masu zanga-zangar sun bukaci shugaba Buhari ya sauka ko kuma su kawo karshen kasar Najeriya. "Tun daga shekarar 1999, 'yan kudancin Najeriya suke cutar da mu game da abinda ya shafi kujerar shugaban kasar Najeriya" "A lokacin da Obasanjo yake shugabancin Najeriya babu wani dan Arewa da ya takura masa har sai da ya kammala wa'adin mulkin sa na shekara 8 a ofis." "Dan uwan mu Yar'Adua yana hawa mulkin Najeriya suka fara sukar gwamnatin sa har sai da ya mutu, a maimakon a dauki wani da...