Posts

Showing posts from October, 2022

MAHAIFI YAYI SANADIYAR CIRE HANNUN DAN SA DAN WATA 2 SABODA YA HANA SHI BACCI A JIHAR IMO.

Image
  Wani mutumi mai suna Mr Amatobi dake jihar Imo yayi ta dukar jaririn shi mai suna Miracle saboda ya hana shi bacci wanda hakan yayi sandiyar yanke hannun jaririn sandiyar raunin da ya samu.  Mahaifiyar yaron ta ce: "abun ya faru ne lokacin da na tashi domin in je in yi fitsari, ko da na dawo na same shi ya ɗaure hannun yaron bayan ya karya shi." Ta ci gaba da cewa; "da na fahimci abunda ya faru sai ya kama ni da jaririn ya rufe mu a cikin daki har tsawon kwana 2. Daga baya Allah Ya taimake ni na fita sannan na nemi mutane su taimaka mani" A lokacin da ta samu fita ta nemi taimakon mutane domin kama wannnan mutumin, inda kungiyar tsaro ta farin kaya ta kama shi amma kuma ya gudu da baya. Bayan ceton su da aka yi an kai yaron asibiti amma saboda rubuwar da hannun yayi dole aka cire shi Baki daya. Kungiyoyi da dama sun yi kira ga jami'an tsaro domin kamo wannan mutumin domin a gurfanar dashi a gaban kuliya.

TAKAITATTUN LABARAN SAFIYAR JUMA'A 4/11/2022 DAGA JARIDAR TAURARUWA HAUSA NEWS KARKASHIN KAMFANIN BELMO MEDIA CONSULT

Image
✅Jami'an tsaro sun fara bincike kan gawarwakin matasa 10 da aka tsinta a Edo. ✅An Fara Gudanar Da Bincike Game Da Cin Zarafin Wani Dan Jarida Da Dan Majalisar Wakilan Najeriya Ya Yi. ✅Tinubu Zai Fara Kaddamar Da Yakin Neman Zabensa A Jihar Filato, Ranar 15 Ga Watan Disamba. ✅Dubban 'Yan Najeriya Ne Suka Samu Kulawa Daga Kungiyar Likitoci Dake Yawo Kasashen Duniya. ✅Idan Na Ci Zabe Zan Sayar wa Da 'Yan kasuwa Duka Matatun Mai Na Kasa – Atiku. ✅Ba Zan Yarda A Samu “Cabal” A Gwamnatinmu Ba – Atiku. ✅NEMA Ta Raba Kayan Abinci Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Borno. ✅An Gurfanar Da Magidanci A Kotu Kan Daba Wa Surukinsa Kwalba. ✅An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Sannan Ya Kashe Yaro Mai Shekara 5 A Kano. ✅Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 44 A Arewacin Najeriya. ✅Gwamnati Ba Ta Sayen Makamai A Wajenmu – Kamfanin Sarrafa Makamai Na Najeriya. ✅Mun Lalata Haramtattun Matatun Mai Sama Da 70 Cikin Mako 2 – Sojoji ✅Miyagun Kwayoyi: NDLEA Ta Cafke Mutum 130 A Kaduna. ✅Dalibai 3,000 Sun...

KIRA NA MUSAMMAN ZUWA GA MAIGIRMA GWAMNA

Image
  Daga Alhaji Bello Ibrahim (Alhajin APC) GYARA KAYAN KA........ Assalamu Alaikum, Bayan gaisuwa irin ta girmamawa zuwa ga Mai Daraja Gwamna. Ya Maigirma Gwamna Hon Dr Bello Matawallen Maradun ina amfani da Wannan damar domin inyi kira akan bashin kuɗin Feeding na Makarantun Sakandare Wanda yanzu an tasarma Shekara ba'a biya ba, abunda ya gurgunta wasu Yan kasuwa sanadiyyar rashin biyan bashin, wasu sun gudu sunbar gidajen su akan wannan bashin, wasu kuma kasuwancin su ya tsaya cikkk duk akan wannan dalilin.  Maigirma Gwamna a Gwamnatocin da suka gabata ba haka aka gudanar da Wannan hulɗar ba.  Maigirma Gwamna Wallahi duk wanda bai faɗa maka cewa akwai illa Mai girma a cikin rashin biyan kudin nan ba to bai faɗa maka gaskiya ba, Wata kila ko ba masoyin ka bane, ko yana jin tsoron ka kasa fahimtar shi, ko kuma tsoron kada yabar samun abunda yake samu.  Maigirma Gwamna rashin biyan bashin nan ba daidai bane kuma yanada illa babba.  Maigirma Gwamna mutanen da ke da...

ABINDA YA FARU GA SIYAMA MAI SHEKARU 3 A DUNIYA

Image
  Daga shafin Abba Hikima Siyama ta rasu ranar Alhamis 29-09- 2022 kimanin karfe 4 na yamma a dalilin  Fyade da wanda ake tuhuma wani Idi  (Baba Idi) mai shekaru kimanin 40 zuwa sama, dake Zaune a Lungun Alhaji Halliru a unguwar Gama, karamar hukumar Nassarawa ya yi mata ranar Talatar da ta gabata. Kimanin kwana shida da ya gabata, Idi ya dauki Siyama zuwa dakinshi ya bata alewa inda ya yi lalata da ita kuma ya tsoratar da ita cewa in dai ta fadawa Abbanta sai ya kasheta da Almakashi kuma ya hadata da magen gidansu ta cinyeta (kasancewar ta mai tsoron mage) ta kwatanta mana yadda ya dora mata almakashi a wuya yace sai ya yankata da shi idan ta fadawa Abbanta. Bayan ta shigo gida an cire mata kaya za ayi mata wanka aka ga jini yana fitowa daga jikinta, aka ce me ya sameta tace "Baba Idi ne yake mun wani abu yauma ya ciremin wando ya yi min ya bani alawa kuma yace idan na fadawa Abbana ze kasheni, Umma don Allah kar ki fadawa Abba". Daga nan aka dauketa aka kaita asibiti in...