Posts

Showing posts from August, 2019

YADDA ZA'A SHIRYAR DA YARA DABI'U MASU KYAU

Image
1. Ku dinga shiga gida da sallama, inda hali ku sumbanci yaran ku, wannan zai sa musu kauna da sanin kiman kan su. 2. Ku zama masu kyakkyawar mu'amala ga makwabtanku, kada ku zama masu gulma da rada, kar ku fadi munanan magana ga masu abin hawa a kan hanya. Yaran ku suna ji, za su koya kuma zasu dauka su dinga yi.  3. Duk lokacin da za kuyi magana da iyayen ku a waya ko za ku ziyarce su ku tabbatar kun yi tare da yaran ku, domin hakan zai sa yara su koyi jin ƙai da kuma tausaya muku don sun ga yadda kuke yi wa naku iyayen. 4. Lokacin kai su makaranta kar ku yawaita sa musu kide kide da waƙoƙin sharholiya, ku yawaita basu labarai da kissoshi da zai ankarar da su Al'amurra na gari, Ina tabbatar muku zai taimaka sosai! 5. Karanta musu guntayen labarai ko wani guntun tarihi a ko wane rana, ba zai ci lokaci ba amma yana taimaka musu wajen nitsuwa kuma yana kama zuciyar su. 6. Ku tsaftace kan ku da Wanka da wanke baki da taje kai da sa kyawawan tufafi (Kaya) ko da kuwa ...

YADDA KALAMAN TSOHON GWAMNA A.A. YARI SUKA RURA WUTA GABA TSAKANIN FULANI DA YAN- SAKAI.

Image
Daga  Khalifa Ja'afar Tun a ranar da Abdulaziz Yari yayi wata dogowar fira mai sa firgici a gidan Radion Kaduna a farkon shekar 2013, inda ya fadi cewa "dukkan kashe-kashe da sace-sace da a keyi a Zamfara fulani ne", hakika, wadannan kalamai sun rura wutar gaba tsakanin Fulani da 'yan sa-kai da sauran al' ummar jihar, domin daga wannan ranar ne fulanin dake zaune a Zamfara aka fara gasa masu aya a hannu, daga wannan ranar basu sake samun walwala da rayuwa mai kyau ba sai a wannan ranar sanadiyar maigirma gwamna, Honorable Bello Muhammad Mutawalle, duk wanda yake a Zamfara yau ya shedi hakan, domin a wannan ranar ne fulani suka samu shiga cikin al'umma kamar yada suka saba tare da gudanar da wasannin su na gargajiya wato (SHARU) a koina a fadin wannan jihar, suka hadu a babban birnin jiha garin Gusau domin gudanar da wannan wasa ta al'ada. Ranar da Abdulaziz Yari ya furta wadannan kazaman kalaman a gidan rediyon Kaduna idan masu bibiyar rubutu na ...