HARIN MAKARANTAR KOYON AIKIN SOJA: Hakika Shugaban kasa Muhammadu Buhari da jami'an tsaron mu sun tafka abin kunya!!
Daga Comrd S-bin Abdallah Sokoto. Idan har 'yan bindiga zasu iya kai farmaki a wannan makaranta ta NDA dake Kaduna to tabbas lamarin tsaro a kasar nan ya yi mummunar lalacewa. Na rantse da idan har Gwamnatin Najeriya bata tashi tsaye ta hallaka wadannan 'yan bindiga ba watatana sai ka ji sun yi garkuwa da Gwamna ko shi kan shi shugaban kasa Muhammadu Buhari din. Hakika wannan hari zai yi matukar cirewa al'ummar karkara tsammanin samun tsaro da suke fatan ganin sun samu a kowace rana ta Allah. Buhari ka ji kunya! Gwamnonin Arewa kun ji kunya! Sanatocin Arewa kun ji kunya!. Maciya amanar Arewa kun ji kunya!. Allah ya isarma talakkan Najeriya da ya sha rana ya zabe ku.